Everton ta dauki aron Mangala

Mangala na cikin tawagar Faransa a gasar cin kofin duniya ta 2014 amma bai buga kowanne wasa ba

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Mangala na cikin tawagar Faransa a gasar cin kofin duniya ta 2014 amma bai buga kowanne wasa ba
An wallafa

Everton ta dauki aron dan kwallon Manchester City Eliaquim Mangala har zuwa karshen kakar bana, inda zai fafata a gasar wasannin Firimiya.

Dan kasar Faransan mai shekara 26 shi ne na uku da kungiyar ta dauka a kasuwar 'yan tamaulan da aka bude ta watan Janairu, bayan Theo Walcott and Cenk Tosun.

Mangala ya koma City daga Porto a shekarar 2014 akan fam miliyan 32, kuma wasa hudu kawai ya buga a gasar Firimiyar bana.

Ya bar kulob din bayan da City ta dauki Aymeric Laporte daga Athletic Bilbao a kan fam miliyan 57.

Mangala ya yi wa City wasa sau 79 tun bayan da ya koma kungiyar daga Portugal, sai dai ya kusan shafe kakar 2016-17 a Valencia yana taka-leda a matsayin aro.